Skip to main content

CAPTAIN SADIQ

*CAPTAIN SADIQ*
            ๐Ÿ‘ฎ๐Ÿผโ€โ™‚

*writing by*
        *Salma mas'ud nadabo*

*Edit by*
    *boold sister deeja*

๐Ÿ“˜ *REAL HAUSA FULANI WRITER'S FORUM*๐Ÿ„

                 1_2

Yarin ya ce yar shekara 10 na hango tana tafe tana rusa kuka kamar anmata mutuwa  Fara ce sosai ita ba siriri ya ba ita ba lukuta ba dan kwallinta ne a hannu ta hakan ya sa na kalli gashin kanta baki sosai amma saboda tsabar datti yayi jawur kallo daya na mai na gane mai laushi rashin kullawa ne yasa yayi haka hancin nan yayi jaga jaga da majina  gata da manyan ido  tana tafe tana kukan dan ba dainawa tayi ba  dai dai wani madai dai cin gida ta tsaya chak gidan kasane gidan tallakawa sosai dan ko kofar gidan bata samu ishashiyar kofa ba  ihu ta Kara saki kamar an watsa mata ruwan zafi inna da ke kurya daki ta fito tana gyara zani inda sabo to ya kamata ta saba da halin fatuha amma ba yadda ta iya dole ta fito inba fitowa tayi ba to wallahi sai  dai maqota su fito ganin inna ta leko yasa fatuha tuna a kasa ta ihu inna ta gyara tsayuwa ohni fatuha nabani yau kuma wakika tsokana kika ci bugu fatuha ciki mirya tsiwa irin na yara masu wayau masu rashin ji ta ce inna wallahi tallahi kwarankwatsi dubu bani na tsokane shi ba inna ta kara rushewa ta saban kuka inna  ta san halin ta sarai shiyasa ta ja bakin  ta tayi shuru to fatuha ways bige ki wallahi inna Rabi'u ne  ya bigeni har da taka min ruwan ciki ta Kara rushewa da saban kuka  kuma inna billahilazi ba zan yadda ba  ta inda zan can tana katse majina hancin ta  saboda inna ta San karya fatuha ba yadda za'ayi rabi'u ya bige ta har ya taka mata ruwan ciki sai dai in laifi ta mai kuma ko bugun ta yayi bai taka mata ruwan ciki qila ma satan mangwaro taje  ya kamata  yi hakuri fatuha ki kyale shi kin ji kuma kiga Rabi'u ba sa'an ki bane kin ji diyar baffan ta kambuuuu ta zaro manya idanuwan ta qur'an inna ban hakura  haba fatuha yi hakuri Zan baki biyar kin ji  washe baki tayi kamar ba ita ke ihu da koke koke ba to inna na hakura kwarankwatsi Inna ta washe baki fatuha ko ba wai rai cikin zuciyar ta ta hakura dan ta dau alwashi se ta Rama bugun da Rabi'u ya Mata haka ta bi inna cikin uwar daka tana matse kwalla da katse majina

    

        Misalin karfe hudu na yamma fatuha ce zaune tsakar gida wadda take share kwal ba dani ko daya da yake inna akwai san tsafta duk yadda ta so ta gyara fatuha da fit a zata Dawo kamar almajira ko sabuwar mahauci ya saboda tsaban rashin ji ko wanka se anyi da gaske inna ke samu ta dirje ta  hura take sha hankali kwance daga gani hura na kai mata karo dan sai rausaya kai take kamar kadangaruwa inna ta ce ta leko daga uwar daka fatuha yi Sauri ki shirya ki tai makaranta allo baki ta turo gaba kamar data tun kudi birji gaskeya yau inna ban zuwa inna na gaji qur'an kullun Malam dalha sai ya bigeni ta inda zan can tana matsar kwalla to fatuha in baki je  makarantar ba inaa zaki sauke baki so na siya maki shanun a yanka ranar sauka washe baki tayi to inna zani wallahi ko dan ki yanka min shanuwa babba tafi tasu fatsima kwarankwatsi yawa yar albarka  maza ki shirya hijabin ta dake saman igiya ta janyo ta zura ta fita da gudu inna ta girgiza kai ta dau kwana hura ta Kai madafi ta aje

    Fatuha da ke tafe tana yan surutai wanda ko ni salma bajin ta nake ba chan ta tsinkayo muryar malam dalha taja birki ta tsaya tana raba ido dan tasan kashin ta ya bushe dan Ba karamar makara tayi ba Malam dalha ne ya juyo sukayi ido 4 da fatuha ya kwallo ido keeeeeeeee!!fatuha dan uban ki yanzu ne lokacin zuwa makaranta shegiya mai Kama da mayu duk kauyan nan kin raina uban kowa yana huci ya ce yau zaki kwafar ubanki wallahi fatuha dake ta raba ido ta duqa da niyar raruma takalmin ta ta ruga miyar Malam dalha ce ta tsinke Mata tunani wallahi kika ruga sai na sa basiru ya dauko min ke akai kasan cewa tasan basiru Ba karamin kato bane yasa taja ta tsaya chafka daya Malam dalha ya Mata yana muzurai kuka ta farayi tana yarfe hannu tana bashi hakuri Allah annabi amma yayi biris ya fisgota ya fara kila kamar an aiko shi ihu take jera mai Allah ya isa bugun ta yake amma bakin yaki mutuwa dan kan shi ya gaji da dukan ta ya hakura fatsima da ke gefe sai matsar kwalla take tana yimai daquwa  ta hijabi ta lalabo gefe fatuha Malam dalha be ganta ba yi hakuri fatuha ki ji Allah sai ya saka maki fatuha dake matsar kwalla ta turo baki gaba  billahilazi sai na rama fatsima ba yana zuwa gidan qilu zan ce ba da yamma ba kwarankwatsin dubu sai nayi maganin shi fatsima Kai fatuha ki kyale shi Dan wallahi ki kai mai iskanci har gida zai biki dan Malam dalha ba wayau garashi ba ya hadaki da baffa yo ni wayau be ya isheni ta karashe zan can tana washe baki fatsima taja bakin ta tayi shuru haka suka cigaba da karatun su dai dai gwargwado fatuha na da kokari sai bata jin magana KO  kadan ba wanda bai san ta akauyan su ba

      Mayan motoci ne kira bentley guda 5 suka nufi wani katafarin gate kallo daya nayi ma motocin na hadiye miyau dai dai katafarin gida motocin suka kunna Kai wurin parking suka nufa suna gama parking da sauri wasu sojoji guda 4 suka daga ciki motar baba at the same time sojojin 4 na cikin mota baya suka nufi  motar tsakiya  ahankali daya daga cikin  sojojin ya bude mai murfin motar tsakiya wani  hadaddden  kafa nagani mai sanye da booth yana cikin kakin shi na sojoji karfafe namijine kyauwa wow fari ne Sol idan sa sanye yake da glass bari wadda ya fido da zala kyan shi da qwarjinin shi dogo ni sosai jikin shi  murde yana da fadandan kirji gashin kanshi mai laushi ne duk da  gashi na cikin hula shi na uniform hakan be hana gashinshi bayyana na ga sajan shi kwance ta hanci shi kamar pencil dan tsini briefcase din shi ya amsa hannu daya daga cikin yaran sa fuskarsa murtuke Ba alamar dariya kamar an aiko mai da wahayin mutuwa na ce ohni Salma da guy dinan zeyi dariya da ba karamin kyau zeyi ba haka yaran suka bashi guri ya wuce Kai tsaya man palour ya nufa wow fadi tsaruwar palour bata lokaci ne saboda ba karamin haduwa yayi ba  baba jinmai da ke gafe cikin washe baki ta tsugunna tana kwasar gaishuwa cikin isa kamar mai koyan magana ya amsa mom fa ah mai gida tana sama Kara daurewa yayi Dan wannan suna kona mai rai yake a hankali yake taka matataka cikin isa  Kai tsaye dakin mom  ya shiga hadaddan daki mai kyau sanyin AC sai ratsa dakin yake hajiya da ke zaune saman kujera dressing mirror tana shafa turare Tasha hadadden leshin ta mai kyau fara ce ba fulata na kallo daya zaka mata kasan Hutu ya zauna mata ahankalin ya karaso yayi huging nata cikin fara'a ta juyo Dan tasan ba mai mata haka se son kiss ya mata mom I miss u miss u more son we'll come back dear baby ka kara girma kamar ba Kai ba turo baki yayi ya langwabe Kai alamar shagwaba Kai mom ni dai  gaskiya ban girma ba ka ji da shi dai kaje kayi wanka ka dawo your food is ready a dinning area ok mom ya fice yana murmushi kamar bashine Wanda kee daurewa dazu Ba

  *Taku har kullu Salma mas'ud nadabo*

Comments

Post a Comment

Popular posts from this blog

Auren Jinsi 1-10

🔴🔵🔴🔵🔴🔵🔴       🔴🔵🔴🔵🔴             🔴🔵🔴                    🔴      AUREN JINSI 🔵🔴🔵🔴🔵🔴🔵      🔴🔵🔴🔵🔴          🔵🔴🔵                🔵     18~2~2018                           Typing..... 01 to 10       Auxxibillahi รƒliyul รƒzim , minรฃl shaddanil r...

Ma'aikaciyar Gwabnati

โ“‚โ“‚โ“‚           MA'AIKACIYAR               GOMNATI               โ“‚โ“‚โ“‚                    1         By Asmabaffa       Masoyana naga sakonku sosai na yabo da jinjina kan novel dina na maraicin rahma,ban San Kalmar da zanyi amfani da ita ba wajen gode muku,na gode kwarai Allah ya bar kauna,Allah ya biya muku dukkanin bukatunku na alkhairi.          LONDON na nufa a 80 jirgi ya saukeni da kyar na hada kudin zuwa ma sabo da jin dadinku readers bazan bari ya wuce Ku ba,wani gida Wanda ya amsa sunansa gida ko a kasar ba duk gida ba,ko ina ya tsaru wani handsome na hango narke a 3seater yana lat...